Daga Mustapha Gambo Muhammad

Hukumar Yaki da Cin Hanci da Rashawa ta Ƙasa (EFCC), ofishin shiyar Kano, ta fara haɗin gwiwa da Hukumar Kula da Zirga-zirgar Ababen Hawa ta Jihar Kano (KAROTA) domin yaki da masu hakar ma’adinai ba bisa ka’ida ba da sauran manyan laifukan tattalin arziki a cikin Jihar Kano da kewaye.

A cikin wani jawabi da Abubakar Ibrahim Sharada Jami’in Hulda da Jama’a na hukumar Karota ta jihar Kano ya sanya wa hannu ranar litinin ya ce wannan haɗin gwiwa ya samu ne a ranar litinin 13 ga Oktoba, 2025, lokacin da Mukaddashin Daraktan Yankin EFCC, DCP Sa’ad Hanafi Sa’ad, ya kai ziyara ta girmamawa ga Manajan Daraktan KAROTA, Hon. Faisal Mahmoud Kabir, a shelkwatar hukumar dake Kano.

Da yake jawabi yayin ziyarar, DCP
Sa’ad ya bayyana cewa KAROTA na da muhimmiyar rawa da za ta taka wajen dakile ayyukan masu hakar ma’adinai ba bisa ka’ida ba, la’akari da yawan ma’aikatanta da kuma yadda ayyukanta suka bazu a manyan hanyoyi da cikin birni.

Ya roƙi hukumar KAROTA da ta taimaka wajen bibiyar hanyoyin da ake amfani da su wajen jigilar ma’adinai da aka samo ba bisa ka’ida ba, yana mai jaddada cewa irin wannan bayanai na sirri za su taimaka wa EFCC wajen kama da gurfanar da masu laifi waɗanda ke janyo asarar kuɗin gwamnati da lalacewar muhalli.

A nasa jawabin, Hon. Faisal Mahmoud, ya tabbatar da cewa KAROTA tana da cikakken shiri na yin aiki tare da EFCC, yana mai cewa hukumar koyaushe tana marawa baya duk wani shiri da zai taimaka wajen kare tattalin arzikin Jihar Kano.

Ya kuma buƙaci hukumar EFCC ta bayyana a hukumance irin bayanan da take buƙata, tare da tabbatar da cewa KAROTA za ta ba da cikakken goyon baya da duk wasu bayanan sirri da za su taimaka wajen tabbatar da nasarar wannan hadin gwiwa.

← Back

Thank you for your response. ✨

Leave a Reply

Your email address will not be published. Required fields are marked *

You May Also Like

Kano Gov’t Assures Its Effort In The Implementation of Land Policies- Commissioner Land

By: Mukhtar Yahaya Shehu The Kano State Commissioner for Land and Physical Planning,…

NLC Pushes for Fresh Minimum Wage Review, Says ₦70,000 No Longer Viable

By: Abdullahi Muhammad Abuja – The Nigeria Labour Congress (NLC), alongside federal…

ISMPH Organizes A Training To Kano Journalists On How To Reduce Maternal Mortality

By: Mukhtar Yahaya Shehu   International society of Media in public Health…

2025 Press Week: NUJ Kano Organizes Capacity Building Workshop to its Members

By: Mukhtar Yahaya Shehu  Nigeria Union of Journalists Kano state council has organised…

World Day Against Trafficking in Persons: AHIP Calls for Stronger Protection of Children, Adolescents, Young People

By: Mukhtar Yahaya Shehu  The Executive Director of the Adolescent Health and Information…

Borno NANNM Commends Governor Zulum for Advancing Frontline Health Workers

By: Kabir Getso  The Borno State branch of the National Association of…

Deputy Senate President Visits Barau FC Training Ground, Donates N2M.

By: Zaharadeen Saleh. The Deputy President of the Senate, Senator Barau I. Jibrin,…

KSCHMA Holds Enrollee Town Hall Meeting at Bunkure PHC to Strengthen Healthcare Delivery

By: Mukhtar Yahaya Shehu  Kano State Contributory Healthcare Management Agency (KSCHMA) has continued…